in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi ya halarci taron dandalin tattaunawar bunkasuwar Sin
2017-03-21 10:41:44 cri
Jiya Litinin, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya halarci babban taron dandalin tattaunawar bunkasuwar kasa ta Sin na shekara-shekara, inda ya ba da jawabi mai taken "gina dangantakar abokantaka cikin hadin gwiwa, da kuma neman bunkasuwa cikin zaman lafiya".

Cikin jawabinsa, Wang Yi ya bayyana cewa, ana ci gaba da fuskantar sauye-sauyen yanayi a fannoni daban daban a duniya, gamayyar kasa da kasa suna sa ran kasar Sin za ta iya ba da gudummawa kan harkokin kare zaman karko da neman ci gaba na kasa da kasa. Haka kuma, kasar Sin tana son sauke nauyin dake wuyanta na ba da gudumawarta cikin himma da kwazo kamar yadda ya kamata, amma ba ta taba yin tunanin cewa, za ta ba da jagoranci kan kasa da kasa ba.

Kasar Sin tana son kulla dangantakar abokantaka dake tsakaninta da kasa da kasa bisa ka'idojin nuna adalci da kuma bude kofa ga waje, yayin da gaggauta gina sabuwar dangantaka da za ta sa a cimma moriyar juna, lamarin da zai ba da taimako wajen cimma burinmu na samun dunkulewar bil Adama.

Bugu da kari, ya ce, kasar Sin za ta karfafa dangantakar abokantaka dake tsakaninta da kasashe masu tasowa, domin ba da taimko da goyon baya ga juna a yayin da aka dukufa wajen neman bunkasuwa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China