in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi taron ministocin harkokin wajen kasashen G20 a Jamus
2017-02-18 12:58:42 cri
A ranar 16 da kuma ranar 17 ga watan nan da muke ciki ne, Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya halarci taron ministocin harkokin waje na kungiyar G20 a birnin Bonn na kasar Jamus.

Inda ya bayyana ra'ayoyi da matsayin kasar Sin kan batutuwan da suka shafi yadda za a aiwatar da jadawalin samun dauwamammen ci gaba na da shekarar 2030, da dangantakar dake tsakanin sauran kasashen duniya da kasashen Afirka, da kuma yadda za a iya kiyaye zaman lafiya a hali mai sarkakiya da aka ciki a nan duniya da dai sauransu.

Wang Yi ya ce, kasar Sin tana sa ran gamayyar kasashe za su kiyaye zaman lafiyar kasa da kasa, yayin da suke kokarin raya tattalin arziki bisa ka'idojin neman ci gaba, da kulla kawance da kuma bada dama ga sauran kasashe, da fahimtar juna, ta yadda za a hada kai wajen samun ci gaba, da kafa sabuwar dangantakar tsakanin kasa da kasa.

Sa'annan, ya yi kira da sanya jadawalin neman dauwamammen ci gaba nan zuwa shekarar 2030, cikin shirin tabbatar da ci gaban kasashen duniya.

A ganin kasar ta Sin, ya kamata a mai da hankali kan kiyaye zaman lafiyar duniya, yayin neman ci gaba da hadin gwiwa, sannan kuma, a girmama ra'ayoyin kasashen Afirka, tare da ba su taimako yadda ya kamata a lokacin da suke dukufa wajen samun ci gaba.

A halin yanzu, kasar Sin tana aiwatar da manufofinta bisa tsare gaskiya da nuna adalci, yayin ba da taimako ta hanyoyin da suka dace ga kasashen Afirka.

Bugu da kari, Wang Yi ya jaddada cewa, kasar Sin ta tsaya tsayin daka, wajen neman bunkasa cikin zaman lafiya, inda ta dukufa kan ayyukan kiyaye zaman lafiyar duniya.

Haka kuma, tana son karfafa hadin gwiwarta da gamayyar kasashe, kan aikin kiyaye zaman lafiya da na tsaron kasa da kasa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China