in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi musayar wuta a tsakanin sojojin gwamnatin Syria da sojojin adawa
2017-03-20 12:29:54 cri
Jiya Lahadi 19 ga wata, sojojin gwamnatin kasar Syria sun yi musayar wuta mai tsanani da 'yan tawayen kasar a wani yankin Jobar dake gabashin Damascus babban birnin kasar, a lokacin da 'yan adawa suka yi kokarin kutsawa birnin, amma sojojin gwamnati suka fatattake su.

Rahotanni sun bayyana cewa, tuni gwamnatin kasar ta kara sojojin da ta tura zuwa wuraren dake kusa da Jobar, inda kuma aka toshe wasu hanyoyin da za su isa yankin.

Kungiyar kare hakkin bil Adama wadda hedkwatarta dake birnin London na kasar Burtaniya, ta bayyana cewa, 'yan tawayen sun harba boma-bomai a wurare da dama dake birnin Damascus, sa'an nan sojojin gwamnatin kasar sun mai da martani gare su ta sama.

Rahotannin sun kara da cewa, yayin gumurzun, sojojin gwamnati sun kashe 'yan tawayen da dama, tare da jikkata wasu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China