in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An share fagen sabon zagayen shawarwari kan batun Syria
2017-03-04 13:20:23 cri
Manzon musamman na babban magatakardan MDD mai kula da batun Syria, Staffan de Mistura, ya bayyana a birnin Geneva na kasar Switzerland a jiya Jumma'a cewa, an kammala wani zagayen tattaunawa tsakanin masu ruwa da tsaki kan batun Syria a Geneva, bayan an shafe kwanaki 9 ana kokarin samun masalaha.

Ya kara da cewa, za kuma a gudanar da wani sabon zagayen tattaunawar bayan wasu kwanaki, a cikin watan nan da muke ciki.

A cewar mista Mistura, duk da cewa ba a samu wani muhimmin sakamako yayin tattaunawar ba, tawagar gwamnatin kasar Syria da masu adawa da gwamnatin, sun cimma matsaya kan abubuwan da za su tattauna a kai a zaman da za a yi nan gaba.

Hakan a cewar Mistura ya shimfida wani kyakkyawan tubali ga tattaunawar da za a gudanar a nan gaba.

Ban da haka kuma, mista Mistura ya ce abubuwan da za a tattauna kansu a nan gaba, sun kunshi batutuwa 4. Cikinsu har da batutuwa 3 da suka shafi mika mulkin kasar, wato su kafa gwamnatin gamin gambiza da gyara kundin tsarin mulki da sake gudanar da babban zabe. Ban da haka kuma aka kara da batun yaki da ta'addanci, bisa bukatar tawagar jami'an gwamnatin kasar Syria.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China