A cikin wata sanarwar da rundunar sojan kasar Siriya ta fitar, an ce, sakamakon goyon-bayan da sojojin saman Rasha da Siriya suka bayar, sojojin Siriya sun fatattaki dakarun kungiyar nan ta IS, lamarin da ya sa suka karbe garin Palmyra gami da kewayensa. A halin yanzu, ana kokarin kawar da abubuwan fashewa da dakarun IS suka dana.
Sanarwar ta ce, sojojin gwamnatin Siriya sun samu ci gaba wajen yakar dakarun kungiyar IS a jihar Aleppo dake arewacin kasar, abun da ya kasance babbar galaba da sojojin gwamnatin kasar suka samu kan dakarun na IS.
Har wa yau kuma, sanarwar ta jaddada cewa, sojojin gwamnatin Siriya gami da sojojin kawancensu, su kadai ne ke iya murkushe ayyukan ta'addanci, za kuma su ci gaba da yaki da kungiyar IS da sauran kungiyoyin 'yan ta'adda.(Murtala Zhang)