in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakataren janar MDD ya yi Allah wadai da hare-haren da aka kai ma Damascus
2017-03-13 10:20:39 cri
A jiya Lahadi ne Antonio Guterres, sakataren janar MDD, ya yi bayar da sanarwa ta bakin hannun kakakinsa, a ranar Lahadi da ta gabata, inda ya yi Allah wadai da hare-haren ta'addanci 2 da aka kai ma birnin Damascus, fadar mulkin kasar Syria, tare da jaddada bukatar ganin an gurfanar da mutanen da suka gudanar dakai wadannan hare-haren a gaban kuliya.

A ranar Asabar da ta gabata ne, an aka kai harin bom ga wasu manyan motoci 2 masu dake dauke da fasinjoji 'yan darikar Sshi'a na kasar Iraki, a birnin Damascus, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane fiye da goma.

Dangane da hare-haren, ma'aikatar harkokin wajen kasar Syria ta mika sako ga babban magatakardan MDD da shugaban kwamitin sulhu na Majalisar, inda ta bukaci Majalisar da ta yi tofin Allah tsine kan wadannan hare-haren bom da suka abku a Damascus. A cewar ma'aikatar, an kai hare-haren ne don ramuwar gayya ga sojojin gwamnatin kasar, wadanda sakamakon suka samu nasarorin da suka samu a kwanakin baya wajen tinkarara a yakin da suke yi da kungiyoyi masu tsattsauran ra'ayi a kwanakin baya. Haka zalika, hare-haren sun nuna yadda 'yan ta'adda dake kasar ba sa son ganin samun masalaha tsakanin al'ummomin kasar, in ji ma'aikatar harkokin wajen kasar Syria.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China