Wata katuwar bishiya ta fada a dab da wata magangarar ruwa a yankin Kintampo a lardin Brong-Ahafo da ke kasar Ghana a ranar 19 ga wata, inda masu yawon shakatawa a kalla 16 suka rasa rayukansu, wadanda yawancinsu 'yan makarantar sakandare ne da ke bude ido a magangarar ruwan, yayin da wasu da dama suka jikkata.
Bayan abkuwar hadarin, masu ba da agaji na wurin sun iso wurin da hadarin ya abku, sun kuma kai wadanda suka ji rauni a asibiti. (Tasallah Yuan)