in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin Shugaban kasar Ghana ya bukaci hadin kan kasashen Afrika wajen raya tattalin arzikin nahiyar
2017-03-08 11:21:02 cri

Mataimakin shugaban kasar Ghana Mahamudu Bawumai, ya bukaci kasashen Afrika su karfafa hadin kai da nufin samun habakar tattalin arzikin yankin cikin sauri.

Mahamudu Bawumai wanda ya yi kiran a jiya Talata, yayin bude wani taron yini biyu na 'yan asalin nahiyar dake zaune a kasashen ketare, ya jadadda bukatar habakar nahiyar ta yadda za ta tsallake matakin samun tallafi daga kasashen duniya zuwa na dogaro da kanta.

Ya ce yadda ake kallon nahiyar a gida da waje ya dogara ne a kan tattalin arzikinta, yana mai cewa, kamata ya yi a hada karfi da karfe don ganin nahiyar ta samu ci gaba ta fuskar tattalin arziki, ta yadda za ta iya tsayawa da kafarta.

Har ila yau, mataimakin shugaban kasar Ghanan ya bukaci kasashen nahiyar su yi koyi da kasar Sin da sauran kasashen nahiyar Asiya, wadanda bisa jajircewa da kwazo, suka kai matakin da suke a yanzu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China