in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Koton kolin Burtaniya ta bukaci May ta tuntubi majalisar kafin ta fara batun ficewa daga EU
2017-01-24 19:51:41 cri
Kotun kolin Burtaniya ta yanke hukuncin cewa, wajibi ne firaminista Theresa May ta tuntubi majalisar dokokin kasar kafin ta fara shirin tattaunawa game da shirin Burtaniyar na ficewa daga kungiyar tarayyar Turai (EU)

Kotun ta sanar da hakan ne a yau Talata, bayan da alkalan kotun kolin suka yanke hukuncin da ya goyi bayan wasu kungiyoyin jama'a da suka kalubalanci matakin gwamnatin Burtaniya wajen amfani da doka ta 50 game da shirin fara tattaunawar ficewarta daga kungiyar tarayyar Turai.

Yanzu matakin kotun kolin kasar ya baiwa 'yan majalisar dokoki damar kada kuri'a kafin fara aiwatar da shirin. Sai dai wannan mataki na kotun kolin bai yi wa gwamnatin dadi ba. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China