A yayin taron, Yang Jiechi ya bayyana cewa, a yayin ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kai kasar Burtaniya a shekarar da ta wuce, shugabannin kasashen biyu sun cimma ra'ayi daya dangane da gina dangantakar abokantaka a tsakanin kasar Sin da kasar Burtaniya bisa manyan tsare-tsare a karni na 21, haka kuma, kasar Sin tana son yin hadin gwiwa da kasar Burtaniya don ganin an aiwatar da ayyukan da shugabannin kasashen biyu suka cimma, ta yadda za a karfafa shawarwari a tsakanin kasashen biyu, da zurfafa fahimtar juna da hadin gwiwa a fannin siyasa, ta yadda za a ciyar da bunkasuwar dangantakar abokantaka a tsakanin kasar Sin da kasar Burtaniya gaba, da ba da gudummawa wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaban duniya baki daya.
A nasa bangare, Boris Johnson ya bayyana cewa, kasar Burtaniya tana tsayawa tsayin daka wajen raya dangantakar abokantaka dake tsakaninta da kasar Sin bisa manyan tsare-tsare, kuma za a shiga "muhimmin lokaci" na raya dangantakar abokantaka a tsakanin kasashen biyu. Kasar Burtaniya tana son karfafa mu'amalar dake tsakaninta da kasar Sin bisa manyan tsare-tsare, domin inganta hadin gwiwar kasashen biyu a fannonin tattalin arziki, zuba jari da ababen more rayuwa da dai sauransu, ta yadda za a fuskanci manyan kalubalolin da duniya ta ke fama da su cikin hadin gwiwa, yayin da karfafa fahimtar juna kan wasu batutuwan kasa da kasa. (Maryam)