in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi garkuwa da ma'aikatan MDD guda biyu a Congo-Kinshasa
2017-03-14 10:23:08 cri
Gwamnatin kasar Congo-Kinshasa ta fidda da wani rahoto a jiya cewa, a daren ranar 12 ga wata, wasu dakaru sun kai hari kan ma'aikatan MDD guda biyu a lardin tsakiyar Kasai na kasar, inda suka yi garkuwa da su.

Kakakin gwamnatin kasar Congo-Kinshasa Lambert Mende ya bayyana cikin rahoton cewa, daya daga cikin ma'aikatan MDD guda biyu da aka yi garkuwa da su Ba-Amurke ne, kana dayan kuma dan kasar Sweden ne, baya ga wadannan ma'aikata biyu, an kuma yi garkuwa da wasu 'yan kasar Congo guda hudu wadanda suka tare da ma'aikatan a lokacin da wannan lamari ya auku.

Gwamnatin kasar Congo da tawagar musamman ta MDD dake aikin kiyaye zaman lafiya a kasar sun dukufa domin ceto wadanda aka yi gurkuwa da su, a sa'i daya kuma, hukumar shari'a tana bincike kan wannan lamari.

Rahotanni na cewa, dakarun dake adawa da gwamnati su kan tayar da hankula a lardin tsakiyar Kasai dake tsakiyar kasar Congo-Kinshasa, don haka, MDD ta tura wata tawagar masana zuwa wurin domin ta yi nazari, ta kuma gabatarwa kwamitin sulhu na MDD rahoto game da yanayin da kasar ke ciki a fannin tsaro. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China