in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministocin harkokin wajen Sin da Jamhuriyar Kongo sun yi wata tattaunawa
2017-01-11 10:59:18 cri

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya gana da takwaransa na Jamhuriyar Kongo Jean Claude Ngakosso jiya Talata 10 ga wata a birnin Brazzaville.

Wang ya ce, dangantakar dake tsakanin Sin da Jamhuriyar Kongo, abar koyi ce ga kasashen dake tasowa a duniya.

Kasar Sin ta bada taimako gami da shiga cikin manyan ayyukan masana'antu da bunkasa tattalin arziki ta hanyoyi daban-daban a kasar ta Kongo.

Kazalika, Wang ya bayyana cewa, kasar Sin ta ba Jamhuriyar Kongo shawarwari game da yankin Pointe-Noire, har ya zamanto wani katafaren aiki na hadin-gwiwar masana'antun Sin da Kongon, da kafa wasu manyan cibiyoyi guda hudu, ciki har da cibiyar jigilar kaya, da cibiyar kere-kere da ta zirga-zirgar jiragen sama da sauransu.

A nasa bangaren, Jean Claude Ngakosso ya nuna cewa, kasar Sin babbar aminiyar cinikayya ce ga Jamhuriyar Kongo, kuma Kongon ta amince da irin ra'ayoyin da gwamnatin kasar Sin ke da su wajen karfafa hadin-gwiwa da ita.

Kongo tana fatan Sin za ta kara taimaka mata wajen raya yankin Pointe-Noire, ta yadda zai samar da alfanu ga al'ummar kasar.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China