in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD da AU da sauran hukumomin kasa da kasa sun yi kira ga bangarorin Congo Kinshasa da su yi hakuri da juna
2016-09-25 12:37:59 cri
A jiya ranar 24 ga wata, MDD da AU da EU da kungiyar kasashe masu amfani da harshen Faransanci sun bayar da hadaddiyar sanarwa, inda suka nuna damuwa kan tashe tashen hankulan da suka faru a birnin Kinshasa na kasar Congo a kwanakin baya, kuma sun yi kira ga bangarori daban daban na kasar da su yi hakuri da juna tare da magance sabanin dake tsakaninsu.

Sanarwar ta bayyana cewa, wadannan hukumomin kasa da kasa hudu sun yi kira ga kungiyoyin siyasa daban daban na kasar Congo Kinshasa da su yi hakuri da juna, da kalubalantar magoya bayansu da su magance tada rikice-rikice. Hukumomin sun bayyana cewa, za su ci gaba da nuna goyon baya ga kasar Congo Kinshasa da ta yi shawarwari a tsakanin 'yan kasar, tare da jaddada cewa, ba a iya aza tubali ga aiwatar da zaben shugaban kasar yadda ya kamata sai idan an cimma daidaito da juna ta hanyar yin shawarwari a tsakanin bangarori daban daban na kasar.

Bisa shirin da aka tsara, za a gudanar da zaben shugaban kasar Congo Kinshasa a ranar 20 ga wannan wata, amma hukumar zaben kasar ta bayyana cewa, kamata ya yi a sabunta rijistan zabe, don haka aka jikirtar da gudanar da zaben. Amma jam'iyyun adawa sun yi watsi da wannan kuduri. Tun daga ranar 19 ga wannan wata, jam'iyyun adawa na kasar sun yi zanga-zanga a birnin Kinshasa, inda masu zanga-zanga fiye da dubu daya suka yi fito na fito tare da jami'an tsaro, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane a kalla 32. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China