in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya jaddada muhimmancin zabe cikin lumana da adalci a RDC-Congo
2016-07-16 17:44:21 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya jaddada a ranar Jumma'a kan muhimmancin gudanar da zabuka cikin lumana da adalci a kasar RDC-Congo, kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada, domin zaman lafiya, ci gaba da kuma karfafa tsarin demokaradiyya a cikin wannan kasa.

A cikin wata sanarwa, kwamitin ya jaddada wajabcin gaggautar dake da akwai wajen kira tattaunawar siyasa da za ta kunshi dukkan bangarorin dake ruwa da tsaki, musammun ma kan maida hankali ga shirya zabuka.

Kwamitin sulhu ya kuma bayyana damuwarsa kan karuwar haramce haramce a dandalin siyasa a kasar RDC-Congo, musammun ma kan kame kamen baya bayan nan na mambobin jam'iyyun sisaya dana kungiyoyin fararen hula. Haka kuma kwamitin ya bayyan babbar damuwarsa kan tauye hakkin jama'a da kuma jinkirin da ake samu wajen shirya zabuka. Kwamitin sulhu ya yi kira ga gwamnatin RDC, da kuma bangarorin da abin ya shafa, da su girmama 'yancin dan Adam da kuma kaucewa tashe tashen hankila da kuma tsokana. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China