in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An halaka dakarun tsaro a yammacin Nijar
2017-03-07 10:23:28 cri
Kafofin watsa labaran Jamhuriyar Nijar sun ce, daga daren Lahadi zuwa sanyin safiyar jiya Litinin, wasu 'yan bindiga dadi da ba'a san ko su wanene ba, sun kai hari kan wani rukunin dakarun tsaro na musamman a yankin Tillabery dake yammacin kasar, lamarin da ya janyo kisan dakarun tsaron kasar a kalla hudu, tare da raunata wasu hudu.

Rahotanni sun ce, an ji karar bindigogi babu tsayawa, kana 'yan bindigan sun gudu bayan da suka kai harin, gami da kone wata motar dakarun tsaro kurmus.

A wani labari daga jami'an tsaron Jamhuriyar Nijar kuma, gwamnatin kasar ta aike da wasu jiragen sama masu saukar ungulu daga birnin Yamai a safiyar jiya Litinin, domin bankado maboyar wadanda suka kai wannan hari.

A 'yan kwanakin nan, yankin yammacin Nijar dake bakin iyakokin kasashen Mali da Burkina Faso, na shan fama da hare-haren ta'addanci, abun da ya sa gwamnatin Nijar ta sanar da ayyana dokar ta baci a wasu jihohi shida dake yankunan Tillabery da Tahoua.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China