in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu 'yan jarida na Afirka sun yabawa tarukan CPPCC da NPC
2017-03-05 17:30:21 cri

Yau ne aka kaddamar da taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin a birnin Beijing.

Yayin bikin kaddamarwar, firaministan gwamnatin kasar Sin Li Keqiang ya gabatar da wani rahoto game da aikin da gwamnatin kasar Sin ta yi a shekarar ta 2016 da kuma wanda za ta yi a bana.

Wasu 'yan jarida na kasashen Afirka da ke daukar rahoton taron dake gudana a birnin Beijing, sun yabawa tarukan 2 na CPPCC da NPC.

Hordel Biakoro daga gidan telibijin na kasar Congo (Brazzaville) ya ce, gwamnatin Sin ta himmantu wajen kawo wa jama'arta ayyukan alkhairi, a kokarinta na inganta walwala da rayuwarsu. Kana Kataka daga kasar Togo ya yaba wa yadda ake gudanar da tarukan 2 yadda ya kamata. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China