in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An wallafawa rahoto game da rawar da Burtaniya ta taka a yakin kasar Iraki
2016-07-06 19:27:42 cri
A yau ne gwamnatin Burtaniya ta wallafa rahoton kwamitin binciken nan da aka kafa game da rawar da kasar ta taka a yakin kasar Iraki,inda kwamitin ya bayyana cewa, Burtaniyar ta shiga yakin ne kafin a kai ga cimma duk wata kafa ta samar da zaman lafiya.

Shugaban kwamitin John Chilcot wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa, ya ce daukar matakin soja ba shi ne matakin karshe da ya dace a dauka a yakin na Iraki ba.

Bugu da kari, kwamitin binciken ya gano cewa,firaministan Burtaniya na wancan lokaci Tony Blair ya shaidawa tsohon shugaban Amurka George Bush watanni da dama kafin su kaddamar da shirin mamaye kasar Iraki cewa,yana tare da shi a kowane hali dangane da kasar ta Iraki. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China