in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a mai da hankali wajen kare hakkin dan Adam, in ji Antonio Guterres
2017-02-28 13:43:19 cri
Babban magatakardan MDD Antonio Guterres ya bayyana cewa, batun kare hakkin dan Adam wani muhimmin batu ne da ya shafi harkoki daban daban, don haka ya kamata a mai da hankali kan wannan batu, kamar yadda aka mai da hankali kan harkokin tattalin arziki, zaman takewar al'umma da kuma 'yancin al'adu.

Mr.Guterres ya bayyana haka ne a yayin da yake jawabi a taron kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD karo na 34 da aka bude a wannan rana, haka zalika ya ce, ya kamata kasashen duniya su nuna adalci game da batutuwan da suka shafi harkokin kare hakkin dan Adam, sabo da ta wannan hanya ce kawai za a karfafa hadin gwiwar kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD ta yadda zai samu amincewa daga al'ummar duniya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China