in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta gabatar da jawabi a taron kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD
2016-03-14 11:19:54 cri
A ran Jumma'ar da ta gabata ne, a madadin kasashe 46 ne mukaddashin zaunannen wakilin kasar Sin dake birnin Geneva Fu Cong, ya gabatar da jawabi mai taken "kyautata ayyukan kiwon lafiyar jama'a domin inganta ikon kiwon lafiya" a taron kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD karo na 31.

Cikin jawabinsa, Fu Cong ya ce kiwon lafiya shi ne tushen kare hakkin dan Adam, yana kuma taimakawa wajen cimma burin kiyaye sauran hakkokin dan Adam. Ya ce al'ummar duniya na da bukatar samun kulawa mai kyau ta fuskar kiwon lafiya, domin jin dadin zaman rayuwa cikin mutunci. Sai dai a hannu guda an sha fama da yaduwar cututtuka da dama a sassan duniya, kamar su cutar kanjamau, da Ebola, da zazzabin cizon sauro da dai sauransu. Ban da wannan kuma, akwai bukatar a yi kokari don rage adadin rasuwa, da rashin lafiyar yara kanana.

Fu ya kara da cewa, akwai bambanci a tsakanin kasashen duniya game da gudanar da ayyukan kiwon lafiyar jama'a. Ya zama dole a inganta harkokin kiwon lafiya, da gina ababen more rayuwa na kasa da kasa, domin kawar da rashin daidaito a tsakanin kasashe daban daban a fannonin samun hidima, da labarai, da ilmi a wannan fanni, musamman ma kamata ya yi a kara kokarin kawar da bambancin da ake nuna wa mutane masu karamin karfi. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China