in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala taron jami'an tsare-tsaren kungiyar BRICS na bana
2017-02-24 20:28:00 cri
A yau Jumma'a ne, a birnin Nanjing na lardin Jiangsu dake gabashin kasar Sin, aka kammala taron farko na jami'an tsare-tsare na kasashen BRICS na shekara ta 2017, wadanda suka hada da Brazil, Rasha, Indiya, China gami da Afirka ta Kudu,.

A yayin taron wanda aka fara a jiya, mahalarta sun mayar da hankali matuka gami da gudanar da shawarwari kan yanayin siyasa da tattalin arziki na duniya, da kuma cimma maslaha kan manyan ayyuka hudu da za su gudanar a bana, wadanda suka hada da, inganta hadin-gwiwa ta fuskokin siyasa, tattalin arziki da kuma mu'amala tsakanin al'umma.

A ranar 1 ga watan Janairun bana ne, kasar Sin ta karbi shugabancin karba-karba na kungiyar BRICS, haka kuma daga ranar 3 zuwa 5 ga watan Satumbar bana, za'a gudanar da taron shugabannin kasashen BRICS karo na 9 a birnin Xiamen na lardin Fujian dake kudu maso gabashin kasar Sin,

A nasu bangaren kuma, wakilai mahalarta taron a wannan karo a birnin Nanjing, sun yabawa rawar da kasar Sin ta taka a matsayinta na shugabar karba-karba ta kungiyar, kana sun yarda da babban jigon taron da aka tsara, gami da batutuwan da za'a tattauna a wajen taron shugabannin kungiyar da za'a yi a watan Satumba a birnin na Xiamen da ke nan kasar Sin.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China