in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta bukaci kasashen BRICS da su zurfafa hadin kai don samun makoma mai kyau
2017-01-01 12:07:02 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping a yau Lahadi, ya yi kira ga mambobi kasashen BRICS, wadanda suka hada da Brazil, Rasha, Indiya, China da kuma Afrika ta kudu, da su zurfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu domin samun kyakkyawar makoma.

Shugaba Xi, ya yi wannan kira ne a sakon da ya aikewa shugaban Rasha Vladimir Putin, da shugaban Afrika ta kudu Jacob Zuma, da shugaban Brazil Michel Temer, da kuma firaministan Indiya Narendra Modi, inda ya gabatar musu da takaitaccen bayani game da cikakken shirin kasar Sin kan yadda za'a bunkasa hadin gwiwar kasashen BRICS a shekarar nan ta 2017.

Shugaban ya ce, kasar Sin ne za ta karbi bakuncin taron kolin na BRICS karo na 9 a Xiamen, wani muhimmin birnin dake kudu maso gabashin kasar Sin a lardin Fujian a watan Satumba. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China