in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen BRICS na son kafa hukumar auna karfin tattalin arziki
2017-02-20 13:23:39 cri
Jaridar 'Business Daily' ta kasar Kenya ta ba da labari a kwanakin baya cewa, kasashe 5 dake cikin kungiyar BRICS, wato Brazil, Rasha, Indiya, Sin da Afirka ta Kudu, suna yunkurin kafa wata hukumar auna karfin tattalin arziki mai zaman kanta.

Jaridar ta ce, an fara gabatar da shawarar kafa hukumar ce a wajen wani taron shugabannin kungiyar BRICS da ya gudana a shekarar 2015, daga bisani aka sake tabbatar da wannan aniyyar a cikin sanarwar da kungiyar ta bayar a Goa na kasar Indiya. A halin yanzu, kungiyar ta sa wasu masanan ilimin hada-hadar kudi da su yi nazari game da dabarun da za a dauka don kafa wannan hukuma.

Bayanai na nuna cewa, ana son kafa wannan hukuma ce domin wasu manyan hukumomin da ke auna karfin tattalin arziki 3 da suka shahara a duniya, wato Standard & Poor, Moody's, da kuma FTICH, dukkan su suna aiki da manufofin da kasashe masu sukuni suka tsara ne. Saboda haka, akwai rashin adalci, yayin da ake auna karfin yanayin tattalin arziki a kasashe masu tasowa, gami da kasashen da tattalin arzikinsu ke bunkasa, lamarin da ya sanya kasashe da yawa yin korafi a kansa.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China