in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin Sudan da masu adawa da gwamnatin na zargin juna da sabawa yarjejeniyar tsagaita bude wuta
2017-02-22 10:23:00 cri

Jiya Talata 21 ga wata, rundunar sojin kasar Sudan da masu adawa da gwamnatin kasar, sun dorawa juna laifin sabawa yarjejeniyar tsagaita bude wuta, da ta hargitsi a jihar Kordofan ta Kudu.

Tun a shekarar 2011 ne Rundunar sojan kasar Sudan ta fara yakar masu adawa da gwamnati wato kungiyar 'yantar da jama'ar Sudan (SPLM).

A watan Yunin 2016 ne, shugaban kasar Omer Hassan Ahmed Al-Bashir ya sanar da tsagaita bude wuta na tsawon watanni 4, inda daga baya kuma, ya yi ta tsawaita wa'adin tsagaita bude wutan.

A ranar 15 ga watan Janairun bana ne gwamnatin kasar Sudan ta tsayar da kudurin ci gaba da tsagaita bude wuta na tsawon watanni 6 a dukkan wuraren kasar da rikici ya shafa. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China