in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Sudan ta kudu za su karfafa hadin gwiwa a fannin kiwon lafiya
2017-02-12 12:29:16 cri
Kasar Sin da Sudan ta kudu sun amince su karfafa dangantakar hadin gwiwa a fannin cigaban kiwon lafiya da musayar kwarewa, da sanin makamar aiki, da kuma tsarin hadin gwiwa tsakanin asibitoci.

Wannan yarjejeniyar wacce aka cimma a Juba a Jumma'ar da ta gabata, za ta baiwa kwararru a fannin kiwon lafiya daga kasar Sin damar bude cibiyoyin gwaje gwaje da na gudanarwa a kasar ta gabashin Afrika.

An cimma wannan yarjejeniyar ce a yayin wata ganawa tskanin manyan jami'an gwamnatin Sudan ta kudu da kuma tawagar kwararrun kiwon lafiya 15 na kasar Sin, wadda ke karkashin shugabantar Wang Yuming, wani babban jami'in hukumar kiwon lafiya da tsara iyali ta lardin Anhui dake gabashin kasar Sin.

Ministan kiwon lafiya na Sudan ta kudu Riek Gai Kok, ya shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, wannan yarjejeniyar wani bangare ne daga cikin tallafin dala miliyan 33 wanda gwamnatin Sin ta alkawartawa sashen lafiya na Sudan ta kudu. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China