in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hadin gwiwar bil Adama ta dace da bunkasuwar Afirka
2017-02-21 13:44:10 cri
A ranar 10 ga wannan watan ne, a taron kwamitin raya zaman takewar al'umma na MDD karo na 55 aka zartas da kudurin raya sabuwar dangantakar abokantaka a tsakanin kasashen Afirka da sauran kasashen duniya, inda a karon farko aka shigar da tunanin gina makomar bil Adama cikin hadin gwiwa cikin kudurin MDD.

A cewar masanan Afirka, wannan manufar da kasar Sin take sa ran za a gudanar da ita, ta dace da bunkasuwar kasashen Afirka, har ma da duk duniya baki daya.

Shehun malami a jami'ar Addis Ababa ta kasar Habasha Konstantinos ya bayyana cewa, bunkasuwar kasashen Afirka baki daya na bukatar kasashen duniya su shiga a dama da su a harkokin zaman lafiya da yin gasa cikin adalci. Tunanin kasar Sin ya dace da bukatar kasashen Afirka wajen shiga harkokin bunkasuwar kasa da kasa a nan gaba.

Bugu da kari, shehun malamin ya ce, a halin yanzu, kasar Sin tana aiwatar da manufar gina makomar bil Adama cikin hadin gwiwa yadda ya kamata, kuma, ana mai da hankali kan dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka. Kana, ko shakka babu, taimakon da kasar Sin ta baiwa kasashen Afirka game da gina ababen more rayuwa, zai warware matsalolin da suke hana bunkasuwar kasashen Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China