in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu jiragen kasa guda biyu sun yi karo da juna a Afirka ta Kudu
2017-02-21 10:33:50 cri
Da misalin karfe 6 na daren jiya Litinin ne wasu jiragen kasa guda biyu, suka yi karo da juna a wani wuri kusa da tashar jirgin kasa ta Lynn Ross dake birnin Pretoria na kasar Afirka ta Kudu, inda mutane sama da 100 suka jikkata.

Kakakin hukumar kula da ayyukan gaggawa na birnin Pretoria John Bidesai ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa hadarin ya haddasa jikkatar mutane tsakanin 100 zuwa 150, kuma 20 daga cikinsu na dauke da raunuka masu tsanani.

Haka kuma, wani mai aikin ceto na hukumar ba da taimakon jinyar gaggawa dake wurin, ya bayyana cewa jiragen biyu sun yi karo ne a kan hanyar jirgin kasa guda daya, sai dai ba a kai ga tantance dalilin da ya haddasa aukuwar hakan ba, kuma ba a san dalilin da ya sanya suka hau layin dogo daya ba.

Hadarin dai ya auku ne a lokacin da mutane ke da matukar yawa a jiragen kasa, kuma a lokacin, an yi ruwan sama a birnin na Pretoria. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China