in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afirka: Masu ruwa da tsaki a fannin makamashi na taro a Johannesburg
2017-02-21 09:55:44 cri
Sassan masu ruwa da tsaki a fannin raya makamashi daga kasashen Afirka daban daban na taro a birnin Johannesburg na Afirka ta kudu.

An dai bude taron wanda aka yiwa lakabi da "Energy Indaba" ne a jiya Litinin, kuma mahalartan sa za su maida hankali sosai, ga zakulo hanyoyin cin moriyar nau'o'in makamashi da kasashen nahiyar ke da su. Wannan taro dai na yini 3 na samu halartar wakilan gwamnatoci, da 'yan kasuwa tare da masu zuba jari.

Da ya ke gabatar da jawabi a yayin bude taron, mataimakin babban darakta, kuma shugaban sashen sarrafa iskar gas na Afirka ta kudu Dr. Garth Strachan, ya ce albarkatun iskar gas da aka gano a kasashen Mozambique, da Angola da kuma Tanzania, za su bada damar samar da karin makamashi a Afirka.

Har wa yau Dr. Strachan ya ce akwai bukatar kasashen nahiyar su hada kai da juna, wajen cin gajiyar fa'idojin dake tattare da makamashin iskar gas. Ya ce sashen na kunshe da damammaki na samar da ayyukan yi, da kuma bunkasa tattalin arzikin daukacin nahiyar ta Afirka.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China