in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron Astana: Kasashen Rasha da Turkiyya da Iran za su sa ido kan tsagaita bude wuta a Siriya
2017-02-17 15:58:07 cri
A jiya Alhamis ne, mataimakin tawagar Rasha wadda ke halartar taron shawarwarin zaman lafiya game da Siriya a birnin Astana na kasar Kazakhstan, Mistan Sergey Vershinin ya bayyana cewa, taron ya amince kasashen Rasha da Turkiyya gami da Iran su kafa wani rukuni na hadin-gwiwa, domin sa ido kan yadda kasar Siriya za ta aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma.

A zantawarsa da wani gidan talabijin a birnin Astana, Mista Vershinin ya ce, ayyukan rukunin sun hada da, sa ido kan yadda ake aiwatar da yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta Siriya, da gudanar da bincika ko gwamnatin Siriya da dakarun da ba sa ga-maciji da gwamnatin suna sabawa yarjejeniyar ko a'a. Ya ce, makasudin kafa wannan rukuni shi ne, kokarin samar da amincewa tsakanin gwamnatin Siriya da dakarun da ke adawa da ita, da kuma ciyar da shawarwarin zuwa gaba. Mista Vershinin ya kara da cewa, kafa wannan rukuni zai taka muhimmiyar rawa wajen farfado da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin kasar Siriya da yankunan dake kewaye da ita.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China