in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar gwamnatin Syria ta nuna shakku game da halascin tsagin 'yan adawa a zaman tattaunawa
2017-01-24 13:34:44 cri
Wakilan gwamnatin Syria dake halartar zaman shulhu a birnin Astana na kasar Kazakhstan, sun nuna shakku game da halascin wakilan 'yan adawa a zaman tattaunawar.

Shugaban tawagar gwamnatin Syria Bashar al-Ja'afari, ya ce kungiyar Jabhat al-Nusra, ta taba kame ikon yankin ruwa dake samarwa al'ummar birnin Damascus ruwan sha, kuma ta sa jama'ar birnin kasa samun ruwan sha har tsawon kwanaki 42. Duk da haka tsagin 'yan adawar basu dauke su a matsayin 'yan ta'adda ba.

Kaza lika Al-Ja'afari ya soki 'yan adawar da murde ma'anar yarjejeniyar tsagaita wuta.

Sai dai a nasa bangare, jagoran wakilan 'yan adawar Mohammed Alloush, cewa yayi halartar wakilan masu tada kayar baya a Syria da kasar Iran ke daukar nauyi bai dace ba, kuma zai sanya a fuskanci matsaloli wajen cimma kudurin tsagaita bude wata.

An dai bude taron shawarwari na birnin Astana ne a jiya Litinin, kuma sassan gwamnatin Syria da 'yan adawa, tare da sauran masu ruwa da tsaki na Rasha da Turkiyya da MDD sun halarci taron.

Kaza lika an gayyaci jakadan Amurka dake Kazakhstan George Krol, domin ya kasance cikin masu sanya ido ga gudanar taron.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China