in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi: Ya kamata a aiwatar da shirin neman ci gaba mai dorewa
2017-02-17 11:14:55 cri
A jiya Alhamis ne, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya halarci taron farko na ministocin harkokin wajen kasashe maso karfin tattalin arziki wato G20 a birnin Bonn na kasar Jamus. A jawabin da ya gabatar dangane da shirin neman ci gaba mai dorewa nan da shekarar 2030, Mr Wang ya shaidawa  cewa, a yayin taron kolin G20 wanda aka yi a birnin Hangzhou na kasar Sin a bara, an mayar da batun neman ci gaba a matsayi mai muhimmancin gaske ga jadawalin kungiyar G20, inda aka zartas da shirin jadawalin neman ci gaba mai dorewa nan da shekarar 2030, wanda kamata yayi a gudanar da shi yadda ya kamata.

Wang ya bada shawarar cewa, na farko, a maida shirin neman ci gaba mai dorewa nan da shekarar 2030 a cikin manyan tsare-tsaren neman ci gaba na kasashen G20, na biyu, a ci gaba da ba da muhimmanci ga batun neman bunkasuwa cikin abubuwan da kasashen G20 za su tattauna a kai, da kuma sanya wannan batu cikin manufofin raya tattalin arziki na kasashen G20. Na uku shi ne, ya kamata kasashen G20 su dauki nauyi kafada da kafada domin neman ci gaba mai dorewa, ta hanyar la'akari da karfin kowace kasa. Wang ya kuma kara da cewa, ya zama dole bangarori daban-daban su ci gaba da nuna kwazo wajen aiwatar da yarjejeniyar Paris da aka daddale dangane da shawo kan matsalar sauyin yanayi.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China