in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakateren harkokin waje Birtaniya ya tabbatar da batun komarwa Gambia kungiyar kasashe renon Ingila wato Commonwealth
2017-02-15 10:29:37 cri
Sakataren harkokin wajen Birtaniya Boris Johnson, ya ce shugaban kasar Gambia Adama Barrow, ya tabbatar masa cewa kasar za ta koma cikin kungiyar kasashe renon Ingila wato Commonwealth.

A shekarar 2013 ne, Tsohon Shugaban kasar Gambia Yahaya Jammeh, ya janye kasar daga kungiyar, yana mai zarginta da ci da gumin kasashe masu tasowa.

Yayin wani taron manema labarai jiya a Banjul, babban birnin kasar Gambia, Boris Johnson ya ce ya gana da shugaba Barrow, yana mai cewa, sabon Shugaban na kyawawan manufofin ciyar da kasar gaba.

Ya ce, yana alfaharin sanar da cewa, Gambia za ta koma kungiyar Commonwealth, inda ya ce ya tattauna da sakatare Janar ta Kungiyar, kuma ta kuduri niyyar gaggauta tabbatar da batun.

A jiya talata ne, sakataren harkokin wajen Birtaniyan ya isa Banjul, a wani bangare na ziyarar kwanaki biyu da ya kai Afrika. Zai kuma isa kasar Ghana, inda aka shirya zai gana da sabon shugaba kasar Nana Akufo- Addo. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China