in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun Nijeriya za su koma gida daga Gambia
2017-02-03 09:34:14 cri
Wani babban Jami'in gwamnatin Nijeriya, ya ce dakarun kasar wadanda ke cikin rundunar hadin gwiwa na kasashen yammacin Afrika dake aikin wanzar da tsaro a Gambia, za su koma gida nan bada dadewa ba.

Shugaban majalisar Dattijan kasar Bukola Saraki ne ya bayyana haka ga manema labarai a babban birnin kasar Abuja, jim kadan bayan wata ganawar sirri da suka yi da Mukaddashin Shugaban kasar Yemi Osinbajo.

Shugaban na majalisar dattiijai da ya samu rakiyar takwaransa na majalisar wakilai Yakubu Dogara, ya ce mukaddashin shugaban kasar ya yi musu karin haske game da ayyukan dakarun Nijeriya a kasar Gambia.

Nijeriya ta tura sojoji dari biyu da jirgin yaki zuwa Senegal, a wani bangare na kokarin tabbatar da sakamakon zaben kasar Gambia.

Sojojin dai, na cikin dakarun hadin gwiwa na kungiyar ECOWAS, da shugabanni kungiyar suka dorawa nauyin shiga tsakani, tare da tabbatar da aiwatar da sakamakon zaben shugaban kasar Gambia da aka yi ranar 1 ga watan Decemban 2016.(Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China