in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta ce shugaban Gambiya ya koma kasarsa
2017-01-27 13:09:40 cri
Kakakin sakatare-janar na Majalisar Dinkin Duniya Stephane Dujarric ya bayyana a jiya cewa, shugaban Gambiya Adama Barrow ya dawo birnin Banjul, fadar mulkin kasar, kuma jami'an MDD za su tallafawa kasar wajen ganin an mika mulki cikin ruwan sanyi.

A zantawarsa da 'yan jaridu, Mista Stephane Dujarric ya bayyana cewa, wakilin musamman na sakatare-janar na MDD mai kula da yammacin Afirka da Sahel, Mohamed Ibn Chambas, ya isa birnin Banjul a ranar Alhamis, inda zai ci gaba da tattaunawa tare da Adama Barrow kan halin da ake ciki a kasar ta Gambiya.

Stephane Dujarric ya kuma ce, Chambas zai yi shawarwari tare da shugaban majalisar dokoki, da wasu tawagogin jami'an diflomasiyya, gami da kungiyoyin fararen-hula na Gambiya, don ya tantance ofishin MDD mai kula da batutuwan yammacin Afirka da Sahel kan yadda zai taka rawa wajen taimakawa Gambiya mika mulki cikin lumana.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China