Guillaume Soro daya ne daga cikin 'yan takara guda biyu, wadanda suka tsaya takarar zaben shugaban majalisar dokokin kasar na wannan karo.
Yayin zaman majalisar dokokin kasar da aka yi a birnin Abidjan, mambobin ta 230 daga jimillar 252 ne suka nuna goyon bayan su ga Guillaume Soro, lamarin da ya ba shi damar lashe zaben shugaban majalisar dokokin kasar. (Maryam)