in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi fatan huldar da ke tsakaninta da Amurka za ta ci gaba da bunkasuwa
2017-01-06 20:39:56 cri

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya bayyana cewa, dorewar kyakkyawar hulda tsakanin kasashen Sin da Amurka, buri ne na bai daya da jama'ar kasashen 2 da ma sauran kasashen duniya ke fatan cimmawa. Mr. Geng ya bayyana hakan ne a yau Jumma'a 6 ga wata a nan birnin Beijing.

Rahotanni na cewa a kwanan baya, sakataren harkokin wajen kasar Amurka John Kerry, ya mika wa shugaba Barack Obama na Amurka rahoton cikar wa'adin aikinsa, inda ya ce yanzu haka, huldar da ke tsakanin Amurka da Sin na da matukar muhimmanci ga Amurka a harkokin diplomasiyya. Don haka, ya kamata kasashen 2 su fadada hadin gwiwarsu, yayin da suke daidaita kalubale da dama a duniya. Har wa yau rahoton ya bayyana cewa, har ya zuwa yanzu akwai sabani a tsakanin kasashen 2 a wasu sassa. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China