in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatar tsaron kasar Sin ta bukaci Amurka da ta daina yin bincike a yankin tekun kasar Sin
2016-12-18 13:20:28 cri
A daren jiya Asabar ne, rundunar sojan ruwa ta Sin ta tarar da na'urar tafiya a karkashin ruwan teku maras matuki ta rundunar sojan ruwa ta Amurka, hukumar watsa labaru ta ma'aikatar tsaron kasar Sin ta jaddada cewa, a cikin dogon lokaci rundunar sojan Amurka su kan tura jiragen ruwa zuwa yankin tekun kasar Sin domin yin bincike a kowace rana. Sin ta nuna kiyayya ga wannan batu, tare da bukatar Amurka da ta daina irin wannan aiki.

Hukumar watsa labarun ta bayyana cewa, a yammacin ranar 15 ga wata, wani jirgin ruwan ceto na rundunar sojan Sin ya tarar da wata na'ura a yankin teku na kudu. Domin yin rigakafi kan illar da wannan na'ura za ta kawo wa tsaron zirga zirgar jiragen ruwa da na mutane, jirgin ruwan ceto na Sin ya yi bincike kan wannan na'ura.

Bayan yin nazari a kai ne, daga bisani an tabbatar da cewa, wannan na'urar tafiya a karkashin ruwan teku maras matukin ta Amurka ce, in ji hukumar watsa labarai ta ma'aikatar tsaron kasar Sin, kuma ta kara da cewa, Sin ta dora niyyar mayar da na'urar zuwa Amurka ta hanya mafi dacewa. Sin da Amurka suna mu'amala kan wannan batu lami lafiya.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China