in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministar harkokin wajen kasar Sin ya zanta da takwaransa na kasar Amurka
2017-01-05 20:54:23 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya zanta da takwaransa na Amurka mista John Kerry ta wayar tarho a Alhamis din nan, kamar yadda tuni aka tsara hakan.

Yayin tattaunawar tasu, mista Kerry ya jaddada muhimmancin huldar dake tsakanin Sin da Amurka. A cewarsa, tsayawa kan manufar kasar Sin daya tak a duniya, ra'ayi ne na bai daya da jam'iyyu 2 na kasar Amurka suka amince de shi, tuni kuma aka rubuta wannan manufa cikin hadaddiyar sanarwa 3 da aka kulla tsakanin Amurka da kasar Sin.

A nasa bangaren, Wang Yi ya ce, nasarorin da aka samu ta hanyar hadin kan kasashen 2, ba su samu cikin sauki ba, don haka ya kamata dukkanin bangarorin 2 su yi kokarin kare wadannan nasarori, don tabbatar da wanzuwar makomar hulda dake tsakanin kasashen 2.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China