in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta kalubalanci Donald Trump da ya fahimci yadda batun Taiwan yake jawo hankali sosai
2016-12-12 20:24:51 cri

A jiya ne, Donald Trump, shugaban kasar Amurka mai jiran gado ya ce, ya fahimci manufar "kasar Sin daya tak a duniya", amma bai san dalilin da ya sa dole ne Amurka ta amince da manufar ba, illa kasashen Amurka da Sin sun cimma daidaito kan batun ciniki da sauran batutuwa.

Dangane da lamarin, Geng Shuang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana yau Litinin cewa, kasar Sin ta kalubalanci sabuwar gwamnatin Amurka da shugaban kasar mai jiran gado da su kara fahimtar yadda batun na Taiwan yake jawo hankali sosai, ta yadda za su ci gaba da bin manufar "kasar Sin daya tak a duniya" da ka'idoji 3 da Sin da Amurka suka amince da su cikin hadin gwiwa, tare da daidaita batutuwan da suka shafi Taiwan, a kokarin magance duk wata matsala ga huldar da ke tsakanin Sin da Amurka. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China