in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a kiyaye dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, in ji shugaban Amurka
2016-12-17 12:57:30 cri
Shugaban kasar Amurka Barack Obama ya bayyana cewa, a halin yanzu, kasar Sin tana ci gaba da ba da muhimmiyar gudummawa cikin harkokin kasa da kasa, shi ya sa, dangantakar dake tsakanin kasar Amurka da kasar Sin tana da muhimmanci kwarai da gaske, har ta fi dangantakar dake tsakanin kasar Amurka da sauran kasashen duniya muhimmanci.

A yayin taron manema labarai na karshen shekarar bana da aka yi a jiya Jumma'a, Mr. Obama ya bayyana cewa, yadda za a kiyaye dangantakar dake tsakanin kasar Sin da Amurka yana da muhimmin tasiri kan tattalin arzikin duniya da kuma tsaron kasar ta Amurka, shi ya sa, idan dangantakar dake tsakanin kasar Amurka da kasar Sin ta lalace, ko kuma kasashen biyu suka samu sabani bisa dukkan fannoni, babu shakka lamarin zai haddasa illa ga kasashen duniya.

Bugu da kari, Mr.Obama ya ba da shawara ga shugaban kasar mai jiran gado Donald Trump cewa, kafin a yi shawarwari da shugabannin kasa da kasa da kuma na shiyya-shiyya, ya kamata a tabbatar da cewa dukkan ma'aikatan gwamnatinsa su kama ayyukansu yadda ya kamata, sa'an nan su saurari shawarwari da gwamnatocin baya su ba su kan manufofin yadda ake gudanar da harkokin diflomasiyya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China