Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya sanar a yau Laraba 4 ga wata a nan Beijing cewa, bisa gayyatar gwamnatin kasar Ghana, mataimakin shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin Wang Zhengwei, wanda ke matsayin manzon musamman na Xi Jinping, shugaban kasar Sin, zai halarci bikin rantsar da sabon shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo, wanda za a gudanar a ranar 7 ga wata a birnin Accra, fadar mulkin kasar ta Ghana. (Tasallah Yuan)