Bisa yarjejeniyar, kamfanin Star Times zai samu iznin tsara shirye-shirye da watsa shirye-shirye game da gasar wasannin kwallon kafa na kasar Ghana a tashar telebijin, da gidan rediyo, da yanar gizo a shekaru 10 masu zuwa. Kamfanin zai kara zuba jari ga tsara shirye-shirye kan gasar wasannin kwallon kafa na Ghana tare da sa kaimi ga yin hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka a fannin wasanni. (Zainab)