in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi murnar ganin an tsagaita bude wuta a Syria
2016-12-30 10:51:26 cri
Manzon musamman kan harkokin Syria, na babban magatakardan MDD Staffan de Mistura, ya bayyana a ranar 29 ga wata cewa, MDD ta yi murnar ganin an tsagaita bude wuta a duk fadin kasar Syria.

Haka kuma, ya ce ana sa ran ceto rayukan fararen hular kasa ta Syria, inda ya ce, tsagaita bude wutar, zai kuma samar da damammaki wajen gudanar da taimakon jin kai a kasar, tare da samar da yanayi mai kyau na gudanar da taron shawarwari kan batutuwan da suka shafi Syria a babban birnin kasar Kazakhstan, Astana.

A dai jiya 29 ga wata ne, rundunar sojan kasar Syria, ta sanar da tsagaita bude wuta a duk fadin kasar, inda kuma sanarwar za ta fara aiki tun daga karfe 12 na daren jiyan.

Sai dai, ba za a dakatar da yaki da kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta IS, da kungiyar Jabhat Fateh al-Sham, da kuma kungiyoyi masu goyon bayansu ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China