in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Syria ta karbe iko da birnin Aleppo
2016-12-23 10:58:42 cri
Jiya Alhamis, rundunar sojan kasar Syria ta fidda wata sanarwa, inda ta bayyana cewa, dukkan dakarun adawa da gwamnati sun janye jiki daga birnin Aleppo dake arewacin kasar, lamarin da ya nuna cewa, a yanzu, gwamnatin kasar ce ke da iko da birnin Aleppo baki daya.

Haka zalika, babbar hedkwatar sojojin gwamnatin kasar Syria, ta bayyana nasarar da aka cimma, a matsayin muhimmin ci gaba, a yaki da kasar ke yi da kungiyoyin ta'addanci da kuma magoyon bayansu, tana mai cewa, lamarin ya ba da gagarumin taimako wajen ci gaba da ayyukan kawo karshen ta'addanci a kasar, tare da 'yantar da ita baki daya.

Bugu da kari, rundunar sojojin kasar Syria ta sake yin kira ga dakaru masu adawa da gwamnati da su ajiye makamansu.

Bisa yarjejeniyar janye jiki da aka cimma a baya, an ce, ya kamata dakaru masu adawa da gwamnati su yanje jiki daga birnin Aleppo bi da bi, zuwa yankin karkara dake yammacin birnin da kuma lardin Idlib dake makwataka da shi, haka kuma, dakarun adawar dake lardin Idlib su yarda fararen hula su fita daga garuruwan Kafraya da Foah, wadanda suke karkashin ikonsu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China