A yau Alhamis ne sojojin gwamnatin kasar Syria suka ayyana tsagaita bude wuta a dukkan fadin kasar, tun daga tsakar daren gobe Jumma'a agogon kasar.
Wata sanarwa da sojojin suka bayar ta bayyana cewa, tsagaita wutar ba ta shafi dakarun Nusra Front dake da alaka da kungiyar al-Qaida da kungiyar IS ba, kungiyoyin da MDD ta ayyana a matsayin kungiyoyin 'yan ta'adda.
Shirin tsagaita bude wutar ya zo ne bayan nasarar da sojojin kasar suka samu a fagagen daga masu yawa.(Ibrahim)