in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a gaggauta sake hawa teburin sulhu kan batun rikicin Syria
2016-12-22 16:00:22 cri
Mataimakin wakilin kasar Sin na din-din-din a MDD Wu Haitao ya bayyana cewa, ya kamata gamayyar kasashe su dukufa wajen samar da damarmakin sake hawa teburin sulhu game da rikicin Syria.

Yayin babban taron MDD karo na 71, an kada kuri'ar kan daftarin gudanar da binciken wadanda suke da alhakin aikata laifuffukan yaki da sauran miyagun laifuffuka a kasar Syria, inda nan take aka zartas da daftarin bayan an samu kuri'un nuna amincewa guda 105, da 15 na rashin amincewa, yayin da kuma wakilai guda 52 suka janye jiki daga kada kuri'ar baki daya.

Haka kuma, a yayin taron, Mr.Wu ya bayyana cewa, rikice-rikicen da suka auku a kasar Syria sun haddasa babbar matsala ga al'ummomin kasar, lamarin da kasar Sin ta koka da shi, tana mai bukatar bangarorin dake rikicin ya shafa su sake hawan teburin sulhu ba tare da bata lokaci ba, ta yadda za a samu damar tallafawa al'ummomin kasar tare da ba su damar cin gajiyar albarkatunsu yadda ya kamata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China