in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara yiwa wadanda suka yi fashin jirgin saman Libya shari'a
2016-12-26 10:26:48 cri
A jiya Lahadi ne aka fara shari'ar mutanen nan su biyu, wadanda aka zarga da yin fashin jirgin saman fasinja na kasar Libya, yayin zaman wata kotu dake Malta. Wannan ne dai karon farko da aka gurfanar da mutanen gaban kotu.

Mutane biyu wato Ahmed Ali mai shekaru 28, da kuma Suhah Mussa mai shekaru 27, dukkansu 'yan kasar Libya ne. An ce da karfe 12 na ranar 25 ga watan nan da muke ciki, 'yan sanda suka iza keyar wadannan mutane kotun ta Malta domin gurfanar da su gaban shari'a.

Ana zargin mutanen biyu da aikata laifuffukan ta'addanci, da satar jirgin sama, da yiwa fasinjojin da suke cikin jirgin saman barazana, da kuma rike makamai na bogi. Ana dai hasashen cewa idan har aka tabbatar da laifukan da ake tuhumar su da aikatawa, za su iya fuskantar daurin rai da rai.

Sai dai mutane biyu su musanta aikata laifukan da ake zargin su a yayin zaman kotun, kuma ya zuwa yanzu, ba su mika bukatar beli ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China