in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Asusun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya, ya amince da fitar da dala miliyan uku domin aikin wanzar da zaman lafiya a kasar Libya
2016-12-14 10:06:22 cri
UNITED NATIONS, Dec. 13 (Xinhua) – Asusun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya, a ranar Talata, ya sanar da amincewa da amfani da dala miliyan uku wajen tabbatar da zaman lafiya a Libya.

A cewar kakakin ofishin na Majalisar Dinkin Duniya, asusun na da nufin samar da wani yanayi na kyautata tsarin siyasa, ta yadda zai kawo karshen rikice-rikice a kasar.

Duk da yarjejeniyar da majalisar Dinkin Duniya ta samar tsakanin jami'yyun adawa na kasar Libya a watan Disamban bara, har yanzu, kasar na ci gaba da fuskantar rarrabuwar kawuna tsakanin gwamnatoci biyu da majalisun dokoki.

Har ila yau, a Ranar Talatar ne, kwamitin sulhu na majalisar Dinkin Duniya ya amince da fadada aikin taimako na majalisar a Libya zuwa watanni tara, wato nan da wata Satumban shekarar 2017.(Faeza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China