in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rasha ta darajanta batun ficewar dakarun 'yan adawa da gwamnatin Syria daga birnin Aleppo
2016-12-16 10:30:42 cri
A jiya Alhamis 15 ga watan nan ne dakaru masu adawa da gwamnatin kasar Syria suka fara janyewa daga birnin Aleppo dake arewacin kasar. Masanan Rasha sun yi sharhi cewa, idan har an gudanar da wannan aiki lami lafiya, hakan zai samar da yanayi mai kyau na gudanar da ayyukan agajin jin kai a wurin daga dukkan fannoni.

Da yake tsokaci game da hakan, mamban kwamitin lura da zamantakewar al'umma na ma'aikatar tsaron kasar Rasha, kana shahararren mai sharhi kan harkokin aikin soja, Igor Korotchenko ya bayyana cewa, mai yiwuwa ne dakarun 'yan adawar Syria za su dauki wasu matakai a yayin da suke janyewa daga yankin. Duk da haka, gwamnatin Rasha na fatan daukacin dakaru masu adawa da gwamnati dake garin Aleppo, ciki har da 'yan kungiyar masu tsattsauran ra'ayi za su janye, domin samar da yanayi mai kyau na aikin jin kai.

Kaza lika babban hafsan hafsoshin rundunar sojan Rasha, Valery Gerasimov ya bayyana cewa, sojojin Syria sun riga sun mamaye kashi 98 bisa dari na yankunan dake birnin Aleppo. Ya ce kawo yanzu, Rasha da Syria suna share fagen warware rikici tsakanin bangarori daban daban na Syria ta hanyar siyasa.

Har ila yau jami'in ya yi kira ga kasashen duniya da su kara kokarin hadin gwiwa, domin yaki da ta'addanci bisa jagorancin MDD. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China