in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana sa ran inganta harkokin daidaito tsakanin maza da mata
2016-12-17 16:57:37 cri
Jiya Jumma'a, aka yi babban taron kasa da kasa da ya shafi harkokin mata da batun talauci mai tsanani a birnin Rome na kasar Italiya, inda halartar taron suka yi kira da a mai da hankali kan inganta harkokin zaman daidai wa daida a tsakanin maza da mata da kuma baiwa mata iko yadda ya kamata, ta yadda za a ba da taimako wajen kawar da talauci mai tsanani da kuma karancin abinci.

Babban sakataren hukumar abinci da ayyukan gona ta MDD Jose Graziano da Silva, ya bayyana a yayin taron cewa, mata suna ba da muhimmiyar gudummawa cikin ayyukan gona, musamman matan dake zaune a yankunan karkara, wadanda suke bada taimako matuka wajen tabbatar da cimma burin samun dauwamammen ci gaba.(Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China