in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta ta bukaci a samar da kudade don yaki da cin zarafi da kuma muzgunawa mata da yara mata
2016-11-26 13:47:09 cri
Ranar 15 ga watan Nuwambar ko wace shekara rana ce da MDD ta ware don tunawa da yaki da cin zarafin mata a duniya.

A sabo da haka, MDD ta fara wani biki na kwanaki 16 da aka yi wa taken "A yi wa duniya adon launin orange, a tara kudade domin yin amfani da su wajen yaki da cin zarafin mata da yara mata", kuma an shirya bikin ne domin kara sanin mutanen kasa da kasa kan harkokin tashe-tashen hankulan da aka yi wa mata, ta yadda za a iya karbar kudade daga wajensu don ba da taimako kan wannan shiri yadda ya kamata.

Haka kuma, bisa kididdigar da MDD ta yi, an ce, kashi daya bisa uku na matan duniya sun taba gamuwa da tashe-tashen hankula da aka aikata musu, kana, galibin mutanen da suka aikata musu irin wannan laifufuka su ne iyalansu.

A halin yanzu, mutanen duniya sun lura da cewa, tashe-tashen hankulan da aka yi wa mata da yara mata, ya kasance mugun laifin keta hakkin dan Adam, lamarin dake kawo barazana wajen kiyaye lafiyar al'ummomin kasa da kasa, yayin da yake haddasa illa ga dauwamammen ci gaban duniya.

Sabo da haka, babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya gabatar da wani jawabi a yayin ranar kawar da tashe-tashen hankula a gida, inda ya bukaci a karfafa yin rigakafi kan irin wannan matsalar, da daukar matakai yadda ya kamata a lokacin da aka aikata laifin muzgunawa mata, kuma akwai abubuwa da dama da za a yi wajen kawar da irin wannan laifi a duniya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China